Shugaban Majalisar Dattawa, Dr Ahmad Lawan, ya taya yara a fadin kasar nan murnar zagayowar ranar yara ta duniya.
Lawan, a wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Mista Ola Awoniyi, ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa an ware ranar 27 ga watan Mayu ne domin jawo hankalin yara kan hakki da halin da yara ke ciki a Najeriya.
Shugaban Majalisar Dattawan ya ce, dole ne al’ummar kasar su ci gaba da kokarin ganin sun shirya wa matasan kasar nan gaba.
Lawan ya yi Allah wadai da dimbin yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar, ya kuma yi kira da a dauki mataki daga gwamnatoci a dukkan matakai, domin sauya lamarin. In ji The Nation.