Kowace rana ta 13 ga watan Fabrairu, rana ce da hukumar raya al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya ta kebe na musamman, domin tunawa da tasirin da kafar rediyo ke yi wajen sauya rayuwar jama’a, da kuma irin rawar da take takawa wajen bayar da bayanan abubuwan da ke faruwa a fadin duniya.
A Najeriya da Nijar Kamaru da Chadi, rediyo na ci gaba da jan zarenta, a matsayin kafa mafi yawan mabiya da ta fi bayar da bayanai ga jama’a.
Kwamaret Bishir Dauda, sakataren kungiyar Muryar Talaka ne a Najeriya, ya shaida wa BBC cewa, a yammacin Afirka rediyo ita ce kafa wadda akasarin al’umma ke saurare da samun ilimi da kuma samun nishadi.
Ya ce“Rediyo na da matukar taimakawa kwarai da gaske, musamma idan a ka yi la’akari da irin shirye-shiryen da ake yi a gidajen rediyon.
Ya kuma ce,”Akwai abubuwa da dama da ni kai na duk da ilimi na, amma sai a rediyo na kara fahimtarsu, kamar misalin shirye-shiryen da suka jibanci kiwon lafiya ko yanayin zamantakewar al’umma”. A cewar Kwamrade Bishir.