Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna Birtaniya, ta yi kira ga gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari da ta tabbatar an kara baiwa mata dama a kasar.
Kungiyar CANUK, wadda ta wakilci daukacin ‘yan Najeriya mazauna kasar Birtaniya, ta bayyana hakan ne a ranar Lahadin nan a sakonta na fatan alheri ga daukacin iyaye mata na Najeriya na bikin ranar mata ta 2023.
A cikin wata sanarwa dauke da sa hannun shugaban kungiyar, Ayo Akinfe, kungiyar ta ce, tana sane da cewa, a na yi wa mata rashin adalci a Najeriya, dangane da maza.
“Idan aka yi la’akari da cewa, iyaye mata su ne ginshiƙi na iyali kuma babu wata al’umma da za ta ci gaba sai dai idan an dauke su, Canuk zai so ya yi amfani da wannan damar don godiya ga dukan iyaye mata a Najeriya,” in ji ta.
“Har ila yau, ba mu da masaniya game da cewa, mafi yawan kuɗin da uwa ke samu ya fi zuwa ga iyali fiye da na maza, wanda hakan ya sa ƙarfafa tattalin arzikin mata ke da muhimmanci.
“Hakazalika, CANUK ba ta manta da gaskiyar lamarin ba duk da cewa kashi 49.3% na al’ummar Najeriya mata ne, bambancin damammaki tsakanin jinsi yana da yawa.
“Misali, yayin da kashi 86.4% na mazan birane a Najeriya ke da ilimi, kashi 59.5% na mata ne, yayin da a yankunan karkara Najeriya, alkaluman ya kai kashi 74% na maza da 35.4% na mata.
“A fadin Najeriya gaba daya, damammakin da mata ke da su sun yi kadan fiye da yadda ya kamata. Misali, mata kalilan ne ke rike da mukaman siyasa da na shugabanci, domin a halin yanzu Sanatoci bakwai ne kawai cikin 109 da ‘yan Majalisar Wakilai 22 daga cikin 360 na Majalisar Wakilai mata ne.