Gwamnatin jihar Katsina a ranar Lahadin nan ta ce, ta kashe zunzurutun kudi har Naira biliyan 70.99, domin biyan fansho da giratuti ga ma’aikatan jiha da kananan hukumomi da suka yi ritaya daga shekarar 2015 zuwa Agusta 2018.
Gwamna Aminu Bello Masari, ya bayyana hakan ne a wajen taron tattaunawa na ranar ma’aikata na shekarar 2022, wanda kungiyar kwadago ta ƙasa NLC reshen jihar da sauran kungiyoyi masu alaka suka shirya.
Ya ce, ana ci gaba da aikin tantancewa da tantance tsofaffin ’yan jihar da kananan hukumomin da suka yi ritaya daga shekarar 2019 zuwa 2020, kuma an amince da Naira biliyan 1.5 don biyan su bayan kammala aikin.
Masari, wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin kwadago, Tanimu Lawal Saulawa, ya ce, gwamnan ya amince da daukar ma’aikata 5,461 a kowane bangare, domin maye gurbin wadanda suka bar aikin gwamnati.