Ƙungiyar Kiristoci ta kasa, Christian Association of Nigeria (CAN), ta ayyana Juma’a, 4 ga watan Nuwamba a matsayin Ranar Addu’o’i ta Ƙasa don nema wa ƙasar mafita a al’amuranta yayin da ake tunkarar babban zaɓe na 2023.
Ƙungiyar ta gayyaci dukkan ‘yan takara Kiristoci a babban zaɓen zuwa wurin taron da za a gudanar a Cibiyar Kiristoci ta Ƙasa da ke Abuja.
“Za mu nemi kariyar Allah daga fitina, da maguɗi, da harzuƙa masu jefa ƙuri’a da kuma sauran laifuka yayin zaɓe mai zuwa,” a cewar sanarwar da CAN ta fitar ranar Laraba.
Ta ƙara da cewa ta shirya taron addu’ar ne “saboda yadda ƙasarmu ke fuskantar ƙalubala a yanzu duk da irin baiwar da Allah ya yi mata na mutane da ma’adanai”.
Mutum fiye da miliyan 90 ne ke da rajistar kaɗa ƙuri’a a Najeriya, kamar yadda hukumar zaɓe INEC ta bayyana, yayin da ‘yan ƙasar za su su zaɓi sabon shugaba a watan Fabarairu bayan kammala wa’adi biyu da Shugaba Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC zai yi a watan Mayun 2023.