fidelitybank

Ranar 30 ga watan Nuwamba za a yi zaben kananan hukumomi Kano

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta reshen jihar Kano ta ayyana 30 ga wtaan Nuwamba a matsayin ranar gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomi.

Wannan ya zo ne bayan hukuncin kotun ƙoli da ya bai wa ƙananan hukumomi ƴancinsu tare da umartar jihohi su samar da shugaban ƙaramar hukumar mai cikakken iko.

A baya-bayan nan ne gwamnatin Kano ta bayyana cewa a shirye take ta gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi ba da daɗewa ba.

Da yake magana da ƴan jarida a Kano, shugaban hukumar, Farfesa Sani Lawal Malumfashi ya ce hukumarsa a shirye take ta gudanar da zaɓen.

Malumfashi ya kuma ce za a yi wa duka ƴan takara gwajin shan miyagun ƙwayoyi kafin su cancanci tsaywa takarar.

A cewar shugaban hukumar, za a yi zaɓen fitar da gwani da mika muhimman takardun ƴan takara daga 6 ga watan Satumba zuwa 18 ga watan Oktoba.

Hukumar za ta saki sunayen ƴan takarar da suka cancanta a ranar 25 ga watan Oktoba.

Jam’iyyun siyasa kuma na da nan da 1 ga watan Nuwamba su sauya ƴan takara.

An gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi na ƙarshe a jihar Kano ranar 16 ga watan Janairun 2021 a ƙananan hukumomi 44 da mazɓu 484.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp