fidelitybank

Ranar 24 jami’ar ABU za ta koma makaranta

Date:

Biyo bayan dakatar da yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU ta yi na tsawon watanni takwas, jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), ta sanar da ranar 24 ga Oktoba, 2022 a matsayin ranar da za ta ci gaba da gudanar da ayyukan ilimi.

Majalisar Dattawa ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ce ta cimma matsayar.

Daraktan hulda da jama’a na Jami’ar, Auwalu Umar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba, inda ya ce an cimma matsayar ne a taron gaggawar da ta gudanar 516 biyo bayan dakatar da yajin aikin da ASUU ta yi.

Sanarwar ta ce, a zamanta na farko a ranar 25 ga watan Nuwamba, 2021, a zamanta 513, majalisar ta amince da ranar, inda ta kara da cewa saboda yajin aikin ASUU da aka tsawaita, a yanzu majalisar ta sauya ranar zuwa 24 ga watan Oktoba 2022.

Ya ce jami’ar za ta koma ranar Litinin, 24 ga watan Oktoba, 2022, inda ta kara da cewa an shawarci dalibai da su lura da sabuwar ranar, saboda za a fara gudanar da harkokin karatu na yau da kullun.

Haka kuma ta yi kira ga daliban da su rike sabuwar kalandar jami’a ta yadda za ta yi musu jagora domin ba za a samu uzuri ga duk dalibin da ya yi biris da ranar da za a ci gaba da karatu ba.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...
X whatsapp