Biyo bayan dakatar da yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU ta yi na tsawon watanni takwas, jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), ta sanar da ranar 24 ga Oktoba, 2022 a matsayin ranar da za ta ci gaba da gudanar da ayyukan ilimi.
Majalisar Dattawa ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ce ta cimma matsayar.
Daraktan hulda da jama’a na Jami’ar, Auwalu Umar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba, inda ya ce an cimma matsayar ne a taron gaggawar da ta gudanar 516 biyo bayan dakatar da yajin aikin da ASUU ta yi.
Sanarwar ta ce, a zamanta na farko a ranar 25 ga watan Nuwamba, 2021, a zamanta 513, majalisar ta amince da ranar, inda ta kara da cewa saboda yajin aikin ASUU da aka tsawaita, a yanzu majalisar ta sauya ranar zuwa 24 ga watan Oktoba 2022.
Ya ce jami’ar za ta koma ranar Litinin, 24 ga watan Oktoba, 2022, inda ta kara da cewa an shawarci dalibai da su lura da sabuwar ranar, saboda za a fara gudanar da harkokin karatu na yau da kullun.
Haka kuma ta yi kira ga daliban da su rike sabuwar kalandar jami’a ta yadda za ta yi musu jagora domin ba za a samu uzuri ga duk dalibin da ya yi biris da ranar da za a ci gaba da karatu ba.