fidelitybank

Ranar 24 jami’ar ABU za ta koma makaranta

Date:

Biyo bayan dakatar da yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU ta yi na tsawon watanni takwas, jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), ta sanar da ranar 24 ga Oktoba, 2022 a matsayin ranar da za ta ci gaba da gudanar da ayyukan ilimi.

Majalisar Dattawa ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ce ta cimma matsayar.

Daraktan hulda da jama’a na Jami’ar, Auwalu Umar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Laraba, inda ya ce an cimma matsayar ne a taron gaggawar da ta gudanar 516 biyo bayan dakatar da yajin aikin da ASUU ta yi.

Sanarwar ta ce, a zamanta na farko a ranar 25 ga watan Nuwamba, 2021, a zamanta 513, majalisar ta amince da ranar, inda ta kara da cewa saboda yajin aikin ASUU da aka tsawaita, a yanzu majalisar ta sauya ranar zuwa 24 ga watan Oktoba 2022.

Ya ce jami’ar za ta koma ranar Litinin, 24 ga watan Oktoba, 2022, inda ta kara da cewa an shawarci dalibai da su lura da sabuwar ranar, saboda za a fara gudanar da harkokin karatu na yau da kullun.

Haka kuma ta yi kira ga daliban da su rike sabuwar kalandar jami’a ta yadda za ta yi musu jagora domin ba za a samu uzuri ga duk dalibin da ya yi biris da ranar da za a ci gaba da karatu ba.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp