fidelitybank

Rakumin Daawa ya kashe wata Jaririya a Afrika Kudu

Date:

Wata jaririya ta rasu bayan da wani rakumin dawa ya tattake ta a wani gandun namun daji a Afirka ta kudu yayin da mahaifiyar jaririyar ke asibiti cikin mawuyacin hali.

Jaririyar ‘yar wata 16 tana tare ne da mahaifiyarta a wani daga cikin gidaje na alfarma da ke gandun daji na Kuleni Game Park a lardin KwaZulu-Natal.

‘Yan-sanda sun gaya wa BBC cewa har yanzu babu cikakken bayani kan yadda lamarin ya faru, amma dai sun fara gudanar da bincike.

Ba abu ne da aka saba gani ba rakumin dawa wanda kusan ga shi nan da yawa a gidajen namun daji da gandun daji a Afirka ta Kudu, ya far ma mutane.

Jami’in ‘yan-sanda Laftana Nqobile Madlala ya gaya wa BBC cewa faruwar abin ke da wuya aka garzaya da uwar da jaririyarta zuwa dakin likita da ke kusa inda a can jaririyar ta rasu.

Ba a dai san takamaimai inda abin ya faru ba a jiya Laraba, a babban gandun wanda yake da masaukin baki na alfarma har guda 14.

Rakumin dawa shi ne dabba mai shayar da nono mafi tsawo a duniya, kuma ba dabba ce da aka sani da fada ba.

Sai dai tamata wadda ita ma idan wani abu ya nemi taba ‘yarta.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An yi wa Dan shekara 7 yankan Rago a Kano

Wasu ɓata gari da ba a san ko su...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Rundunar Æ´an sanda ta jihar Kano ta ce, ta...
X whatsapp