fidelitybank

Rahoton Reuters na zubar da ciki babu ƙanshin gaskiya – Sojoji

Date:

Kamfanin dilancin labaran Reuters ya ce, ya samu shaidu da ke tabbatar da cewa sojojin Najeriya sun rinka ɓarar da juna-biyu ga mata na tsawon shekara 9, musaman mata da Boko Haram ke yi wa ciki.

Galibin waɗannan matan Boko Haram ne suka yi garkuwa da su da kuma yi musu Fyaɗe a yankunan arewa maso gabashin Najeriya.

Sai dai rundunar sojin Najeriya ta musanta wannan zargi.

Rahoto na Reuters na cewa shirin na ɓarar da cikin mata – akalla mata dubu 10 aka ɓararwa ciki ba tare da amincewarsu ba.

Reuters ya tattauna da mata 33 da ‘yan mata da suka shaida yada aka tilasta cire musu cikin da suke ɗauke da shi, a lokacin da suke riƙe a hannun sojoji.

Matan sun ce ana yi musu allurai da ɗura musu magunguna ɓarar da ciki.

Kafar labaran ta kuma tattauna da wasu jami’an kiwon lafiya biyar da na tsaro 9 da ake gudanar da wannan aikin da su.

An dai ɓarar da galibin wannan ciki ne a cikin watan Nuwamban bara.

Sai dai kamfanin labaran bai iya tantace ko tabbatar da sojojin ko gwamnatin da ta kirkiri wannan shiri na ɓarar da cikin matan ba.

A makon da ya gabata, kafin fitar da wannan rahoton, ma’aikatar tsaro ta ƙasa ta yi fatali da binciken Reuters ta na mai cewa babu gaskiya a ciki, kuma cin mutunci ne ga al’ummar Najeriya da al’adunsu.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp