fidelitybank

Rahoton Amnesty na ikirarin mun kashe masu zanga-zanga 13 ƙarya ne – Ƴan Sanda

Date:

Rundunar ‘yansanda ta karyata wani rahoto da kungiyar kare hakkin dan’Adam ta Amnesty International ta fitar da ke cewa an kashe mutum 13 a yayin zanga-zangar da ake yi a kasar, wadda aka fara ranar Alhamis 1 ga watan Agustan nan.

Haka kuma rundunar a musanta ikirarin da kungiyar ta yi na cewa da gangan jami’an tsaro suna amfani da dabaru don kashe mutane, a yayin da suke kula da taruka tare kuma da amfani da bindigogi wajen tarwatsa zanga-zanga.

Dangane da alkaluman mutanen da suka mutu, wanda rundunar ta karyata na kungiyar ta ce gabadaya mutanen da aka rasa a lokacin zanga-zangar bakwai ne, wasu ba ma a sanadin zanga-zangar ba ma suka mutu.

A sanarwar da kakakin ‘yansandan na kasa, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ya ce, a tsawon kwana biyu na zanga-zangar, mutum hudu sun mutu, talatin da hudu kuma suka samu raunuka a jihar Borno a wani hari na ‘yan ta’adda da ake zargin ‘yan Boko Haram ne.

Sannan ya ce wasu mutum biyu kuma a masu zanga-zanga sun mutu bayan da wani mai mota kirar Honda ya kutsa cikinsu, kuma yanzu haka ana neman direban wanda ya tsere ya bar motar.

Ya kara da cewa can a karamar hukumar Yauri da ke jihar Kebbi kuma wani dan kungiyar sa-kai ta bijilanti ya harbi wani daga cikin masu zanga-zanga da suke satar kayan mutane, inda mutumin ya mutu.

Kakakin ya ce bayan wadannan da ya bayyana mutum bakwai babu wani da ya mutu a lokacin zanga-zangar.

Sai dai an samu yadda wasu ke fashi da makami da barnatawa da satar kayan jama’a da na hukuma da sauransu a lokacin a cewar kakakin.

Rundunar ta kuma karya cewa jami’anta na amfani da bindiga, inda kakakin ya ce jami’ansu na aiki cikin tsanaki da kwarewa kamar yadda ya kamata, suna amfani da hayaki mai sa hawaye ne kawai domin tarwatsa jama’a idan abu ya yi kamari.

Rundunar ta kuma ce mutanen da ta kama ta tsare a lokacin zanga-zangar, ba wai kama su ta yi ba, kawai ta rike su ne tana gudanar da bincike.

A don haka ta yi gargadi kan bayar da bayanan da ba na gaskiya ba a kan zanga-zangar.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp