fidelitybank

Rahoton Amnesty na ikirarin mun kashe masu zanga-zanga 13 ƙarya ne – Ƴan Sanda

Date:

Rundunar ‘yansanda ta karyata wani rahoto da kungiyar kare hakkin dan’Adam ta Amnesty International ta fitar da ke cewa an kashe mutum 13 a yayin zanga-zangar da ake yi a kasar, wadda aka fara ranar Alhamis 1 ga watan Agustan nan.

Haka kuma rundunar a musanta ikirarin da kungiyar ta yi na cewa da gangan jami’an tsaro suna amfani da dabaru don kashe mutane, a yayin da suke kula da taruka tare kuma da amfani da bindigogi wajen tarwatsa zanga-zanga.

Dangane da alkaluman mutanen da suka mutu, wanda rundunar ta karyata na kungiyar ta ce gabadaya mutanen da aka rasa a lokacin zanga-zangar bakwai ne, wasu ba ma a sanadin zanga-zangar ba ma suka mutu.

A sanarwar da kakakin ‘yansandan na kasa, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ya ce, a tsawon kwana biyu na zanga-zangar, mutum hudu sun mutu, talatin da hudu kuma suka samu raunuka a jihar Borno a wani hari na ‘yan ta’adda da ake zargin ‘yan Boko Haram ne.

Sannan ya ce wasu mutum biyu kuma a masu zanga-zanga sun mutu bayan da wani mai mota kirar Honda ya kutsa cikinsu, kuma yanzu haka ana neman direban wanda ya tsere ya bar motar.

Ya kara da cewa can a karamar hukumar Yauri da ke jihar Kebbi kuma wani dan kungiyar sa-kai ta bijilanti ya harbi wani daga cikin masu zanga-zanga da suke satar kayan mutane, inda mutumin ya mutu.

Kakakin ya ce bayan wadannan da ya bayyana mutum bakwai babu wani da ya mutu a lokacin zanga-zangar.

Sai dai an samu yadda wasu ke fashi da makami da barnatawa da satar kayan jama’a da na hukuma da sauransu a lokacin a cewar kakakin.

Rundunar ta kuma karya cewa jami’anta na amfani da bindiga, inda kakakin ya ce jami’ansu na aiki cikin tsanaki da kwarewa kamar yadda ya kamata, suna amfani da hayaki mai sa hawaye ne kawai domin tarwatsa jama’a idan abu ya yi kamari.

Rundunar ta kuma ce mutanen da ta kama ta tsare a lokacin zanga-zangar, ba wai kama su ta yi ba, kawai ta rike su ne tana gudanar da bincike.

A don haka ta yi gargadi kan bayar da bayanan da ba na gaskiya ba a kan zanga-zangar.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp