Yanzu haka dai Super Eagles na iya kara shirye-shiryen tunkarar wasannin sada zumunta da za su yi da Ghana da Mali bayan isowar dukkan ‘yan wasan da aka gayyata.
‘Yan wasa shida da suka hada da Wilfred Ndidi, Kelechi Iheanacho, Frank Onyeka, Francis Uzoho, Chidozie Awaziem da Bright Osayi-Samuel duk sun isa sansanin kungiyar a ranar Laraba (yau).
Kocin rikon kwarya, Finidi George yanzu yana da dukkan ‘yan wasa 22 da aka gayyata a hannunsa.
Ana sa ran sabbin ‘yan wasan za su yi atisaye tare da takwarorinsu a yammacin Laraba.
Za a fara zaman da ake sa ran zai dauki tsawon awa daya da karfe 4:30 na yamma agogon kasa.
‘Yan wasan sune:
Stanley Nwabali, Ojo Olorunleke, Jamilu Collins, Bruno Onyemaechi, Semi Ajayi, Calvin Bassey, Benjamin Tanino, Alhassan Yusuf, Alex Iwobi , Fisayo Dele -Bashiru, Raphael Onyedika,
Ademola Lookman, Moses Simon, Cyriel Dessers, Sadiq Umar, Nathan Tella,
Wilfred Ndidi, Frank Onyeka, Francis Uzoho, Bright Osayi-Samuel, Kelechi Iheanacho, Chidozie Awaziem