Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce, rabon kayan abinci da ake yi a jihar ba na ‘yan jam’iyyar APC kadai ba ne, na dukkan ‘yan jihar ne.
Buni ya bayyana haka ne a lokacin da yake kaddamar da rabon kayan abinci iri-iri ga matsugunai 3,000 a Damagum, hedikwatar karamar hukumar Fune ta jihar.
Gwamnan ya bayyana cewa, domin tabbatar da daidaito da adalci, kwamitin jihar ya kunshi shugaban jam’iyyun adawa, Nigerian Labour Congress, (NLC), Trade Union Congress, (TUC), Nigeria Union of Teachers, (NUT).
Sauran sun hada da kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Najeriya, (NULGE), kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ), kungiyoyin farar hula da kuma wakilan nakasassu da dai sauransu.
Ya kara da cewa dalilin raba kayan tallafin shine don rage wahalhalun da ake samu sakamakon cire tallafin man fetur.
“Cire tallafin man fetur da shugaban kasa Bola Tinubu ya yi ba wai don ya cutar da Najeriya ba ne, sai dai don sanya kasar nan a matsayi mai kyau na ci gaban tattalin arziki mai dorewa”, in ji shi.
Gwamna Buni ya kuma yi gargadin cewa an bullo da hanyoyin da kwamitin rabon kayayyakin da aka raba domin tantance wadanda za su sayar da kayayyakin da aka raba
An tattaro cewa mutane 400,000 a fadin kananan hukumomi 17 na jihar ne ake shirin yin hakan.