Shahararren mawakin Najeriya, Oluwatobiloba Daniel Anidugbe, wanda aka fi sani da Kizz Daniel, ya yi wani rubutut wanda ya bayyana asalinsa a matsayin kabilar Fulani.
Tauraron haifaffen Ogun ya bar mutane da yawa cikin kaduwa bayan ya bayyana ta hannun sa na X ranar Talata cewa shi Bafulatani ne.
“Don haka….Ni rabin Bafullatani ne, rabin Yarbawa,” ya rubuta.
Duk da cewa Kizz Daniel bai fadi asalinsa ba, yawancin magoya bayansa da suka mayar da martani ta bangaren sharhi, suna zargin cewa al’adun Fulani na mawakin na iya kasancewa ta bangaren mahaifiyarsa.