Rasha na shirin mamaye yankuna hudu a Ukraine bayan bayyana sakamakon zaben raba gardama mai cike da cece-kuce.
Zaben na tantance ko yankunan na son zama wani bangare na Rasha na fuskantar tofin Allah tsine daga kasashen Turai.
A Zaporizhzhia, jami’ai sun sanar da cewa kashi 93.11 na masu jefa kuri’a sun goyi bayan yunkurin shiga Rasha.
A Kherson, hukumomi sun ce sama da kashi 87.05 na masu zabe sun bayyana goyon bayansu ta hanyar kuri’u.
A Lugansk, jami’ai sun yi iÆ™irarin cewa fiye da kashi 98.42 cikin É—ari sun amince da haÉ—in gwiwar.
A Donetsk, hukumomi sun ce nasarar ta kusa cika da kashi 99.23 bisa dari na goyon bayan hadewar.
Shugaba Vladimir Putin ya ba da wata alama cewa Kremlin ta shirya karbar cikakken ikon yankunan.
“Ceto mutane a yankunan da wannan kuri’ar raba gardama ke faruwa… shine abin da ya fi mayar da hankali ga daukacin al’ummarmu da ma kasar baki daya”, in ji shi.
Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip ErdoÄŸan zai tattauna da Putin game da ci gaban da Ukraine ta samu.
Erdogan ya bayyana cewa shugaban kasar Volodymyr Zelensky ya bukaci goyon bayan Turkiyya ga yankunan da abin ya shafa da kuma ” shawo kan Putin.”
“Ina fata ba za su gudanar da zaben raba gardama ba kuma a maimakon haka za mu iya magance matsalar ta hanyar diflomasiyya”, in ji shi.
Turkiyya wacce mamba ce a kungiyar tsaro ta NATO tana da kyakkyawar alaka da kasashen biyu da ke yaki tun a karshen watan Fabrairu.