fidelitybank

Raba Gardama: Yankuna 4 na Ukraine na shirin komawa hannun Rasha

Date:

Rasha na shirin mamaye yankuna hudu a Ukraine bayan bayyana sakamakon zaben raba gardama mai cike da cece-kuce.

Zaben na tantance ko yankunan na son zama wani bangare na Rasha na fuskantar tofin Allah tsine daga kasashen Turai.

A Zaporizhzhia, jami’ai sun sanar da cewa kashi 93.11 na masu jefa kuri’a sun goyi bayan yunkurin shiga Rasha.

A Kherson, hukumomi sun ce sama da kashi 87.05 na masu zabe sun bayyana goyon bayansu ta hanyar kuri’u.

A Lugansk, jami’ai sun yi iÆ™irarin cewa fiye da kashi 98.42 cikin É—ari sun amince da haÉ—in gwiwar.

A Donetsk, hukumomi sun ce nasarar ta kusa cika da kashi 99.23 bisa dari na goyon bayan hadewar.

Shugaba Vladimir Putin ya ba da wata alama cewa Kremlin ta shirya karbar cikakken ikon yankunan.

“Ceto mutane a yankunan da wannan kuri’ar raba gardama ke faruwa… shine abin da ya fi mayar da hankali ga daukacin al’ummarmu da ma kasar baki daya”, in ji shi.

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip ErdoÄŸan zai tattauna da Putin game da ci gaban da Ukraine ta samu.

Erdogan ya bayyana cewa shugaban kasar Volodymyr Zelensky ya bukaci goyon bayan Turkiyya ga yankunan da abin ya shafa da kuma ” shawo kan Putin.”

“Ina fata ba za su gudanar da zaben raba gardama ba kuma a maimakon haka za mu iya magance matsalar ta hanyar diflomasiyya”, in ji shi.

Turkiyya wacce mamba ce a kungiyar tsaro ta NATO tana da kyakkyawar alaka da kasashen biyu da ke yaki tun a karshen watan Fabrairu.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp