Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kai ziyarar gani da ido zuwa kauyen Maharba a karamar hukumar Matazu, bayan harin ‘yan bindiga da ya yi sanadin mutuwar Kwamandan Community Watch Corps, Malam Sanusi, da wasu jami’ansa huɗu.
Tawagar Gwamnan ta haɗa da manyan jami’an tsaro da shugabannin gwamnati, inda suka duba wurin da aka kai harin, inda motar jami’an tsaron ta kone baki ɗaya.
Gwamna Radda ya jaddada kudurin gwamnatinsa na ƙara tsaurara matakan tsaro da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro da al’umma. Ya kuma yi ta’aziyya ga iyalan mamatan, yana rokon Allah ya jikan su.