fidelitybank

Raɗɗa ya ƙaddamar da asibiti wanda Mata da Yara za su amfani kyauta

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya ƙaddamar da asibitin kulawa da marasa lafiya kyauta, musamman mata masu juna biyu da ƙananan yara a babban birnin jihar.

Asibitin wanda wata gidauniyar taimaka wa al’umma ta Maiwada Global ta gina, an samar da shi ne a cikin birnin na Katsina.

Wanda ya gina asibitin, Haruna Maiwada ya ce an samar da asibitin ne “Domin tallafa wa a’ummar yankin da magani da kulawa kyauta”.

Gwamnan jihar, Dikko Radda ya bayyana cewa, gina asibitin zai taimaka wa ƙoƙarin gwamnati na inganta lafiyar al’umma da rage wahalhalun da jama’a ke fuskanta wajen samun magunguna da kulawar ƙwarrarun likitoci.

Katsina na daga cikin jihohin da ƙananan yara ke fama da matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki wanda ke haifar da tamowa.

Ƙungiyar likitoci masu bayar da agaji ta ƙasa da ƙasa (MSF), a cikin wani rahoto da ta fitar cikin wannan wata na Disamba, ta ce matsalar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin ƙananan yara a wasu yankunan jihar ta Katsina “ya nunka idan aka kwatanta da bara”.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...
X whatsapp