Ƙasar Qatar ta dakatar da ayyukan da take yi na mai shiga tsakani wajen cimma tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas, kamar yadda jami’ai suka shaida.
Ƙasar ta ce za ta koma mai shiga tsakanin ne kawai idan ɓangarorin biyu suka “nuna sha’awarsu” ta cimma yin tattaunawar.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa Amurka ta nemi ka da Qatar ta sake amince wa da kasancewar wakilan Hamas a Qatar, inda ta zargi ƙungiyar da ƙin amincewa da sabon daftarin yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin.