Gareth Bale na shirin jagorantar Wales wajen kafa wani gagarumin tarihi na buga gasar Kofin Duniya a karon farko cikin shekara 64.
A ranar Litinin ne Wales za ta kara da Amurka a wasan rukuni na biyu a gasar da aka fara bugawa a Qatar ranar Lahadi.
Duk da cewa Wales ta samu halartar gasar kwallon kafar Turai sau biyu a baya-bayan nan, amma ƙasar ba ta samu damar buga gasar Kofin Duniya ba tun shekarar 1958.
“Samun gurbin buga gasar Kofin Duniya wani babban nasara ce ga Æ™asarmu, wani abu ne da Æ™asarmu ke fatan samu tun shekara 64 da suka gabata”, in ji Bale.