Zakarun Ligue 1, Paris Saint-Germain za ta farfado da sha’awarta ta siyan Victor Osimhen a watan Janairu.
A cewar kafar labaran Faransa, RMC Sport, PSG ta riga ta tuntubi wakilan Osimhen.
An danganta kungiyar Luis Enrique da dan wasan na Najeriya a bazarar da ta gabata amma ya ki biyan Yuro miliyan 100 da Napoli ta kayyade.
Dan wasan mai karfi a halin yanzu yana zaman aro a zakarun Super Lig na Turkiyya, Galatasaray.
Dan wasan mai shekaru 25, duk da haka yana da wata ka’ida a kwantiraginsa wanda zai ba shi damar komawa wani kulob a lokacin bazara.
PSG za ta bukaci ta siyar da Randal Kolo Muani domin ta samu damar siyan tsohon dan wasan na Lille.
Osimhen ya ci kwallaye 10 sannan ya taimaka biyar a wasanni 14 da ya buga wa Galatasaray.