Shugaban kungiyar Napoli, Aurelio De Laurentiis, ya bayyana cewa kungiyar ta Ligue 1, Paris Saint-Germain ita ce kungiyar da za ta iya sayen dan wasanta Victor Osimhen a wannan bazarar.
Kungiyoyin kwallon kafa na Turai da dama na sha’awar sayen dan wasan mai shekaru 24, wanda ya zura kwallaye 26 a wasanni 32 da ya buga a dukkanin wasannin da ya buga a kakar wasan da ta wuce.
A cewar Transfermarkt, darajar Osimhen ita ce €120m.
De Laurentiis ya yi imanin PSG za ta iya haifar da batun sakin dan wasan.
Ya ce shugaban Paris Saint-Germain, Nasser Al Khelaifi yana so ya aika da tayin Yuro miliyan 200 kan Osimhen.
“Kungiyar da za ta iya biyan Victor Osimhen ita ce Paris Saint-Germain,” kamar yadda ya shaida wa Mediaset.
“Idan Nasser Al Khelaifi yana so ya aika a tayin kusan €200m… muna jira mu ga abin da zai faru.”
Shugaban Napoli, ya ce yana fatan ajiye Osimhen a kungiyar.