fidelitybank

PRP ta nada Jega a matsayin shugaban kwamaitin yakin zaben gwamnan Kebbi

Date:

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attairu Jega ya zama shugaban kwamitin yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar PRP a jihar Kebbi a zaben 2023 mai zuwa.

A ranar Asabar din da ta gabata ne aka kaddamar da Jega da ‘yan majalisar yakin neman zabensa a Birnin Kebbi wanda ya samu halartan shugabannin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki da kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar Alhaji Abubakar Udu Idris.

A lokacin da yake jawabi ga ’yan majalisar yakin neman zaben dan takarar gwamna na jam’iyyar, Alhaji Abubakar Udu Idris ya shaida musu cewa, su kasance masu gaskiya da sanin yakamata a yakin neman zabe.

A cewarsa, “Na yi imani ba shakka za ku yarda da ni cewa alhakin da aka dora wa Majalisar Yakin Neman Zaben Gwamnan Jihar ta PRP ba abu ne mai sauki ba. Amma , Ina da yakinin cewa sun yi daidai da aikin.

A jawabinsa na karbar shugaban kamfen din takarar gwamna a jihar, Farfesa Attairu Jega, wanda yayi magana ta hanyar zoom, ya yiwa masu ruwa da tsaki da ‘ya’yan jam’iyyar alkawarin za su yi aiki tukuru domin ganin jam’iyyar PRP ta lashe zaben gwamna da sauran zabukan shekarar 2023. a cikin jihar.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp