Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attairu Jega ya zama shugaban kwamitin yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar PRP a jihar Kebbi a zaben 2023 mai zuwa.
A ranar Asabar din da ta gabata ne aka kaddamar da Jega da ‘yan majalisar yakin neman zabensa a Birnin Kebbi wanda ya samu halartan shugabannin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki da kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar Alhaji Abubakar Udu Idris.
A lokacin da yake jawabi ga ’yan majalisar yakin neman zaben dan takarar gwamna na jam’iyyar, Alhaji Abubakar Udu Idris ya shaida musu cewa, su kasance masu gaskiya da sanin yakamata a yakin neman zabe.
A cewarsa, “Na yi imani ba shakka za ku yarda da ni cewa alhakin da aka dora wa Majalisar Yakin Neman Zaben Gwamnan Jihar ta PRP ba abu ne mai sauki ba. Amma , Ina da yakinin cewa sun yi daidai da aikin.
A jawabinsa na karbar shugaban kamfen din takarar gwamna a jihar, Farfesa Attairu Jega, wanda yayi magana ta hanyar zoom, ya yiwa masu ruwa da tsaki da ‘ya’yan jam’iyyar alkawarin za su yi aiki tukuru domin ganin jam’iyyar PRP ta lashe zaben gwamna da sauran zabukan shekarar 2023. a cikin jihar.