Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga Isra’ila a cikin kwanaki masu zuwa sakamakon hare-haren da ke faruwa tsakanin Iran da Isra’ila.
Yayin da take jawabi a wani taron manema labarai, Mataimakiyar ministar harkokin wajen ƙasar, Henryka Moscicka-Dendys ta ce galibi wadanda za a kwashen masu yawon buɗe-idanu ne.
“Mutanen da za mu kwashe sun haɗa da waɗanda suka maƙale a Isra’ila ne a matsayin yawon bude ido ko kuma na ɗan gajeren zama kawai,” in ji ta.
Ta ƙara da cewa za a fara jigilar mutanen zuwa birnin Amman na ƙasar Jordan a titi, sannan daga nan su tashi zuwa Warsaw, babban birnin Poland, saboda rufe sararin samaniyar Isra’ila.