fidelitybank

Poland ta amince da Rasha a matsayin ‘yan ta’adda

Date:

‘Yan majalisar dokokin Poland, sun kada kuri’a kan wani kudiri na ayyana kasar Rasha a matsayin kasar ‘yan ta’adda sakamakon yakin da ta ke yi a Ukraine.

Kudurin wanda ya gudana a ranar Larabar da ta gabata ya samu kuri’u 85, inda ya kara da cewa ya yi kakkausar suka ga cin zarafi na Rasha.

Idan za a iya tunawa dai gwamnatin kasar Rasha karkashin Vladimir Putin ta mamaye kasar Ukraine a ranar 14 ga watan Fabrairun wannan shekara, wanda ya kai ga kazamin yakin da ya yi sanadin mutuwar daruruwan mutane da kuma tasirin tattalin arzikin duniya.

A farkon wannan watan, Putin ya kuma ba da sanarwar shigar da yankuna hudu na Ukraine cikin Rasha. Matakin da shugabannin duniya da dama suka yi Allah wadai da shi.

Sai dai ‘yan majalisar dokokin kasar Poland sun yi kira ga dukkan kasashen da ke goyon bayan zaman lafiya da dimokuradiyya da ‘yancin dan Adam da su amince da hukumomin Tarayyar Rasha a matsayin gwamnatin ‘yan ta’adda.

‘Yan majalisar a yayin da suke zartar da kudurin, sun bayyana bayanan azabtarwa, korar da aka yi musu tilas, da kisan fararen hula da kuma kai hare-hare da gangan kan wuraren farar hula, domin nuna goyon bayansu ga kiran da suka yi na bayyana Rasha a matsayin kasa mai daukar nauyin ta’addanci.

“Mun san duk wadannan ayyukan ta’addancin gwamnati da kyau daga litattafan tarihi,” in ji sanarwar da ke kunshe da kudurin.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp