Tsohon dan wasan baya na Barcelona, Gerard Pique, ya bayyana shirin komawa fagen kwallon kafa a matsayin koci.
Pique ya bayyana hakan ne ta shafinsa na Twitter a ranar Talata.
Dan wasan mai shekaru 36 ya yi ritaya daga taka leda a watan Janairun 2023.
Sai dai a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Pique ya bayyana muradinsa na komawa fagen kwallon kafa a matsayin koci.
“Bayan tunani mai yawa a wannan sabuwar shekara, na yanke shawarar cewa ina so in koma wasan da na ke kewarsa sosai.
“A wannan karon, ba a matsayin dan wasa ba, amma shiga cikin horarwa. Zan raba ƙarin cikakkun bayanai a ƙarshen mako, ”Piqué ya rubuta.
Pique ya buga wa Barcelona wasanni 616 a lokacin da ya ke haskawa a fagen wasa, inda ya lashe gasar La Liga sau tara, da Copa del Rey sau bakwai, da gasar cin kofin duniya na kungiyoyin kwallon kafa na duniya sau uku, da kuma gasar cin kofin zakarun Turai sau uku, daya daga cikinsu yana tare da Manchester United.
Har ila yau, yana cikin tawagar Spain da ta lashe gasar cin kofin duniya ta 2010 da kuma gasar cin kofin nahiyar Turai ta 2012.