Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ta miƙa sakon ta’aziyya ga iyalan tsohon ɗan wasan gabanta David Ebuka, wanda ya mutu a birnin Makurɗi bayan gajeriyar jinya.
A saƙon ta’aziyyar da jami’in hulɗa da jama’a na ƙungiyar Rilwanu Idris Malikawa ya fitar a madadin muƙaddashin shugaban ƙungiyar, da ‘yan wasan ƙungiyar, da sauran ma’aikatan ƙungiyar da magoya bayansu, ya bayyana kaɗuwar ƙungiyar game da rasuwar matashin haziƙin ɗan wasan.
Mista Malikawa ya ce sunan ɗan wasan zai ci gaba da kasancewa a zuciyar ƙungiyar da magoya bayanta.
Ebuka ya koma ƙungiyar Kano Pillars ne a shekarar 2019, kuma yana daga cikin ‘yan wasan da suka taimaka wa ƙungiyar lashe kofin Aiteo Cup a shekarar 2020.