Kungiyar Kano Pillars ta kafa wani kwamiti da zai binciki yadda kungiyar ta kasa samun nasara a wasanni biyu da ta buga a gasar cin kofin kwallon kafa ta Najeriya.
Kwamitin mai mutum biyar yana karkashin jagorancin Rabi’u Muhammad da Alhaji Bashir Baba Chilla a matsayin sakatare.
Kungiyar Sai Masu-Gida ta yi rashin nasara a wasansu na karshe na rukuni-rukuni da Kastina United da ci 1-0, sannan kuma ta sha kashi a wasan karshe da ci 2-0 a hannun Heartland.
Sakamakon bai yi dai-dai da shugabannin kungiyar ba duba da irin kwazon ‘yan wasan da kwararren dan wasan Kano Pillars Evans Ogenyi ya nuna.
Kano Pillars ta samu nasarar zuwa gasar Firimiya ta Najeriya tare da Katsina United daga kungiyar Northern Conference Group.