Dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Rivers a 2015, Dr Dakuku Peterside ya sake caccakar gwamna Nyesom Wike, kan yadda ya kasa biyan kudin fansho na wasu wadanda suka yi ritaya a jihar, duk kuwa da rokon da wasu manyan al’umma ke yi.
Peterside, tsohon shugaban hukumar NIMASA ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar biyo bayan zanga-zangar da wasu masu ritaya suka yi a gwamnatin jihar Rivers a ranar Laraba.
Wadanda suka yi ritaya sun roki gwamnan da ya biya su kudaden fansho, gratuity da duk wasu alawus-alawus din su.
A cikin sanarwar, Peterside ya bayyana cewa tun a shekarar 2015 lokacin da Gwamna Wike ya hau kan karagar mulki, masu ritaya sun yi zanga-zanga a duk shekara, wasu kuma na kwanaki suna kira da a biya su hakki.
Tsohon dan takarar gwamnan ya bayyana Wike a matsayin “mugu, mai taurin kai da rashin hankali” saboda ya ki biyan wadanda suka yi aikin ci gaban jihar duk tsawon rayuwarsu.