An bayyana wanda ya assasa Jami’ar Baze da ke Abuja, Sanata Datti Baba-Ahmed a matsayin wanda zai tsaya takarar mataimakin ,shugaban kasa a jam’iyyar Labour a zaben 2023, Peter Obi.
Dan shekaru 46 kuma tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta Arewa, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter a daren ranar Alhamis.
A cewar sa, “Na yi farin ciki da Mista @PeterObi ya zabe ni a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023 ta hanyar jam’iyyar Labour Party.
“Ina tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa, za mu kafa wata babbar runduna wadda za ta samar da shugabanci nagari, rikon amana da kuma gaskiya.”
Sanarwar ta zo ne sa’o’i kadan bayan wani jigo a jam’iyyar kuma tsohon mai magana da yawun, Doyin Okupe, ya janye aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar mataimakin shugaban kasa, a karkashin jam’iyyar LP.