fidelitybank

Peter Obi ya shigar da karar Tinubu gaban kotu

Date:

Ɗan takarar shugaban ƙasa da aka kammala a watan jiya a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Peter Obi, ya shigar da ƙara a hukumance, inda yake ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasar da ya bai wa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC nasara.

Mista Obi ya shigar da ƙarar ne a kotun sauraron korafe-korafen zaɓen shugaban ƙasa da ke Abuja a ranar Litinin.

Hukumar zaɓen ƙasar dai ta sanar da Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar a matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar.

Masu sa ido kan zaɓen na cikin da wajen ƙasar dai sun ce zaɓen na cike da kura-kurai.

Hukumar INEC ta tabbatar da cewa an samu matsala wajen amfani da na’urorinta, wanda kuma ya shafi aikewa da sakamakon zaɓen zuwa shafinta na yanar gizo.

Mai magana da yawun kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar ta Labour, Yunusa Tanko, ya shaida wa BBC a ranar Talata cewa cikin abubuwan da suke ƙalubalanta dangane da zaɓen sun haɗa da rashin cancantar shiga zaɓe na ɗan takarar jam’iyyar APC.

“Ɗan takararmu ya gabatar da ƙorafe-ƙorafe da dama gaban lauyoyi. Abu na farko shi ne rashin cancantar tsayawa zaɓe na ɗan takarar jam’iyyar APC. Kundin tsarin mulki ya yi tanadin cewa sai mutum yana da takardun makaranta kafin ya tsaya takara. Akwai kuma tuhumar da ake masa a Amurka,” in ji mista Yunusa.

Ya kuma ce ana aza ayar tambaya kan yadda aka gudanar da zaɓen da kuma sanar da wanda ya yi nasara da INEC ta yi.

Peter Obi shi ya zo na uku a zaɓen da aka gudanar yayin da ɗan takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya zo na biyu.

Dukkansu dai suna kalubalantar sakamakon zaɓen saboda zargin da suka yi na cewa yana cike da kura-kur

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp