Ɗan takarar shugaban ƙasa ƙarƙashin jam’iyyar Labour Peter Obi, ya kaɗa kuri’arsa a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.
‘Yan jarida ne suka cika rumfar zaɓen dan takarar da ke Agulu, domin ɗaukar yadda Obi zai kaɗa kuri’ar.
Karanta Wannan: Tinubu ya kaɗa kuri’arsa a jihar Legas
Mista Obi, ana masa kallon shi ne mutum na uku mai tarin magoya baya da suke neman takarar shugabancin ƙasar.
Kamar sauran ‘yan takarar Obi ma ya halarci wajen zaɓen tare da uwar gidansa.