Shahararren mawakin nan, Peter Okoye na kungiyar P-Square ya gargadi ‘yan Najeriya kan yaudarar jam’iyyar All Progressives Congress, APC a zaben shugaban kasa mai zuwa.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter da aka tabbatar a ranar Lahadi, Peter Square ya yi nuni da cewa, da jam’iyya mai mulki ta san mafita kan kalubalen da ke addabar kasar, da sun bayar da ita.
Idan za a iya tunawa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinibu da abokin takararsa, Kashim Shettima, sun sha gaya wa ‘yan Nijeriya cewa, gwamnatinsu za ta kawo karshen dukkan kalubalen da kasar ke fuskanta idan aka zabe shi a shekarar 2023.
Sai dai dandalin Peter Square yayin da yake musanta ikirarin nasu, ya bukaci ‘yan Najeriya musamman masu zabe da su yi amfani da hankalinsu.
Ya bukaci ‘yan Najeriya da su marawa dan takarar jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi baya wanda a cewarsa ya fi iya aiki.
Ya rubuta cewa, “Idan da wata APC ta samu mafita da sun taimaki APC mai ci a cikin rudaninsu. Hankali ne kawai.