Kocin Super Eagles, Jose Peseiro, ya fitar da jerin sunayen ‘yan wasansa na 11 a wasan sada zumunta da za su yi da Guinea.
Kungiyar Syli Stars za ta kara da Super Eagles a wasan sada zumunta na karshe kafin gasar cin kofin Afrika ta 2023 a filin wasa na Bani Yas, Abu Dhabi a ranar Litinin (yau).
Za a fara wasan ne da karfe 1 na rana agogon Najeriya.
Kungiyar Jose Peseiro ta yi wa kungiyar Al Gharib 12-0 ranar Lahadi.
Ana sa ran wasan da Guinea zai zama zakaran gwajin dafi ga Super Eagles.
Hakanan zai zama wata dama ga Peseiro don tantance tawagarsa bayan kusan mako guda na horo mai zurfi a Abu Dhabi.
Ga jerin jadawalin Najeriya don wasan:
23 Nwabali (GK)
3 Zaidu
5 Ekong (C)
12 Osayi-Samuel
22 Umaru
20 Awazim
4 Abdullahi
25 Onyedika
11 Chukwueze
15 Saminu
19 Sadiq
‘Yan jiran ko ta kwana
1.Uzoho, 16.0jo, 2. Aina,
6.Ajayi, 7.Musa, 8.Onyeka
9.0simhen, 10. Aribo
13.Onyemaechi 17.Iwobi
18.Lookman, 21.Bassey