fidelitybank

PDP za ta tantance ‘yan takarar shugaban kasa 17 da suka sayi fom

Date:

‘Yan takarar shugaban kasa 17 a karkashin jam’iyyar PDP za su san makomarsu a yau, yayin da za su fuskanci kwamitin tantance su, domin tantance cancantarsu ko akasin haka.

An shirya gudanar da atisayen ne a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da aka fi sani da Legacy House da ke Maitama, Abuja.

Duk ‘yan takarar da suka biya Naira miliyan 40, domin nuna sha’awa da kuma siyan fom din tsayawa takarar jam’iyyar maza ne, sai dai guda daya da ya biya Naira miliyan 5 kacal a wani mataki da shugabannin jam’iyyar suka tsara domin karfafa gwiwar mata.

‘Yan takarar su ne Teriela Oliver Diana, mace daya tilo; tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar; tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi; Gwamna Nyesom Wike (Rivers), Udom Emmanuel (Akwa Ibom), Bala Mohammed (Bauchi) da Aminu Tambuwal (Sokoto); tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Anyim Pius Anyim.

Sauran ‘yan takarar sun hada da tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose; tsohon Manajan Darakta na FSB, Muhammed HayatuDeen; Likitan da ke zaune a Amurka, Nwachukwu Anakwenze; hamshakin dan jarida, Dele Momodu; wani mai harhada magunguna, Sam Ohuabunwa; tsohon kakakin majalisar dokokin Abia, Cosmos Ndukwe da Charles Ugwu da Honorabul Chikwendu Kalu.

Tuni dai ‘yan takarar suka kara zage damtse wajen ganin sun samu goyon bayan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar musamman wakilan zabe a babban taron kasa da ke tafe.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp