‘Yan takarar shugaban kasa 17 a karkashin jam’iyyar PDP za su san makomarsu a yau, yayin da za su fuskanci kwamitin tantance su, domin tantance cancantarsu ko akasin haka.
An shirya gudanar da atisayen ne a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da aka fi sani da Legacy House da ke Maitama, Abuja.
Duk ‘yan takarar da suka biya Naira miliyan 40, domin nuna sha’awa da kuma siyan fom din tsayawa takarar jam’iyyar maza ne, sai dai guda daya da ya biya Naira miliyan 5 kacal a wani mataki da shugabannin jam’iyyar suka tsara domin karfafa gwiwar mata.
‘Yan takarar su ne Teriela Oliver Diana, mace daya tilo; tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar; tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi; Gwamna Nyesom Wike (Rivers), Udom Emmanuel (Akwa Ibom), Bala Mohammed (Bauchi) da Aminu Tambuwal (Sokoto); tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Anyim Pius Anyim.
Sauran ‘yan takarar sun hada da tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose; tsohon Manajan Darakta na FSB, Muhammed HayatuDeen; Likitan da ke zaune a Amurka, Nwachukwu Anakwenze; hamshakin dan jarida, Dele Momodu; wani mai harhada magunguna, Sam Ohuabunwa; tsohon kakakin majalisar dokokin Abia, Cosmos Ndukwe da Charles Ugwu da Honorabul Chikwendu Kalu.
Tuni dai ‘yan takarar suka kara zage damtse wajen ganin sun samu goyon bayan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar musamman wakilan zabe a babban taron kasa da ke tafe.