Gabanin zaben shugaban kasa na 2023, tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na kasa Cif Olabode George, ya gargadi jam’iyyar adawa da su yi watsi da ra’ayin yin tsarin shiyyar da jam’iyyar ta yi.
George, wanda ya yi wannan gargadin a lokacin da ya gana da wasu ‘yan jarida a Legas ranar Juma’a, ya dage cewa, PDP za ta rasa amanar ‘yan Najeriya idan ta sabawa sashe na 7 karamin sashe na 3 (c) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar.
Sai dai kuma Gwamnan jihar Ondo wanda ya taba zama gwamnan mulkin soji, ya kuma yi gargadin cewa, jam’iyyar za ta yi asara matuka, musamman a zabe mai zuwa, idan har ta kasa sanya tikitin takarar shugaban kasa a yankin Kudancin kasar nan.
Jigon na PDP ya lura cewa, bisa tsarin adalci, dole ne jam’iyyar adawa ta yi abin da ya dace, kuma a cewarsa, ke ware tikitin takarar shugabancin jam’iyyar zuwa yankin Kudu.
Ya kuma bukaci shugabannin jam’iyyar da su fito da tabbatacciyar sanarwa cewa, za a mayar da shugabancin jam’iyyar zuwa Kudu, yana mai cewa ta haka ne kawai jam’iyyar za ta sake samun amincewar ‘yan Nijeriya.