Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mukhtar Yero, ya bukaci masu ruwa da tsaki a jam’iyyar PDP, su hada kai domin baiwa jam’iyyar damar lashe zabe a babban zaben 2023 mai zuwa.
Yero ya yi wannan kiran ne a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa ranar Lahadi a Kaduna.
Ya ce, ya zama wajibi ‘ya’yan jam’iyyar su hada kai, domin samun nasara a zabe mai zuwa a kasar nan.
“Yana da muhimmanci dangin PDP su hada kai domin ceto kasar.
“Dole ne mu nisantar da duk wani daci, mu ajiye muradun kashin kai a gefe, mu duba muradin ‘yan Nijeriya baki daya da kuma jam’iyyar.