fidelitybank

PDP za ta iya hukunta Wike – Umar Sani

Date:

Umar Sani, babban mai ba tsohon mataimakin shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, ga Namadi Sambo, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP za ta iya ladabtar da ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike.

Sani ya ce kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar PDP ya farka kan nauyin da ya rataya a wuyansa kuma yana iya sanyawa Wike takunkumi saboda bai fi karfin jam’iyyar ba.

Da yake magana a shirin safe na gidan talabijin na Arise TV, Sani ya ce babu wani kwamiti da aka kafa a lokacin da ake zargin Wike.

Sai dai ya bayyana cewa da kafa kwamitin ladabtarwa karkashin jagorancin Cif Tom Ikimi, jam’iyyar za ta iya yin la’akari da daukar mataki a kan wadanda ke karya dokokin jam’iyyar.

Sani ya ce: “An yi wa al’amarin sauki sosai, inda da yawa ke kallon lamarin a matsayin rikici tsakanin Abubakar Atiku da Nyesom Wike.

“Amma ainihin abin da ke motsa shi shine kungiyar gwamnonin, wacce ta kasance a kwance amma yanzu ta farka. Dandalin yana aiki tukuru don warware rikicin.

“Duk da cewa umarnin kotu na iya hana tsige jami’ai, hakan bai hana jam’iyyar dakatar da mambobinta ko kuma sanya ladabtarwa ba.

“Babu wani kwamitin ladabtarwa lokacin da ake zargin Wike ya saba wa dokokin jam’iyya.

“Yanzu muna da kwamiti, bari mu ba su lokaci don yin aikinsu kafin a ce Wike ya fi karfin jam’iyya. Mu duba ko sun bada shawarar daukar matakin ladabtarwa a kansa.”

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp