Umar Sani, babban mai ba tsohon mataimakin shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, ga Namadi Sambo, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP za ta iya ladabtar da ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike.
Sani ya ce kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar PDP ya farka kan nauyin da ya rataya a wuyansa kuma yana iya sanyawa Wike takunkumi saboda bai fi karfin jam’iyyar ba.
Da yake magana a shirin safe na gidan talabijin na Arise TV, Sani ya ce babu wani kwamiti da aka kafa a lokacin da ake zargin Wike.
Sai dai ya bayyana cewa da kafa kwamitin ladabtarwa karkashin jagorancin Cif Tom Ikimi, jam’iyyar za ta iya yin la’akari da daukar mataki a kan wadanda ke karya dokokin jam’iyyar.
Sani ya ce: “An yi wa al’amarin sauki sosai, inda da yawa ke kallon lamarin a matsayin rikici tsakanin Abubakar Atiku da Nyesom Wike.
“Amma ainihin abin da ke motsa shi shine kungiyar gwamnonin, wacce ta kasance a kwance amma yanzu ta farka. Dandalin yana aiki tukuru don warware rikicin.
“Duk da cewa umarnin kotu na iya hana tsige jami’ai, hakan bai hana jam’iyyar dakatar da mambobinta ko kuma sanya ladabtarwa ba.
“Babu wani kwamitin ladabtarwa lokacin da ake zargin Wike ya saba wa dokokin jam’iyya.
“Yanzu muna da kwamiti, bari mu ba su lokaci don yin aikinsu kafin a ce Wike ya fi karfin jam’iyya. Mu duba ko sun bada shawarar daukar matakin ladabtarwa a kansa.”