fidelitybank

PDP za ta dawo kan ganiyarta – Bode George

Date:

Wani jigon jam’iyyar PDP, Bode George, ya bayyana fatansa na komawar jam’iyyar kan ganiya.

George ya sha alwashin tabbatar da cewa jam’iyyar PDP ta dawo da martabarta, don haka ya bukaci mambobin su dage.

Rikici ya kunno kai daga jam’iyyar PDP bayan da dan takararta na shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana tsohon gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takararsa a zaben 2023.

Matakin da Atiku ya dauka ya sa tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya jagoranci gwamnonin G-5 da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka bukaci tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu ya yi murabus.

Kiran da suka yi na cire Ayu shine don a samu daidaiton yankin tunda shi da Atiku duk ‘yan Arewa ne.

Sai dai George ya ce za a yi kokarin ciyar da PDP gaba.

Da yake jawabi a babban taron jam’iyyar PDP a Legas, George ya ba da tabbacin cewa duk da abin da ya faru a zabukan da ya gabata, ‘yan PDP su tsaya tsayin daka domin ba za a bar su su mutu ba.

Ya ce: “Ina roƙonku duka, da kuka kasance masu aminci, ku dage; za mu tabbatar da cewa jam’iyyar ta dawo da martabar da ta bata.”

Ya ba da tabbacin cewa, a lokacin da ya dace, dole ne shugabannin jam’iyyar na kasa su gudanar da “cikakkiyar binciken gawarwaki domin warware duk wasu matsalolin da suka shafi jam’iyyar.”

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp