fidelitybank

PDP ta zama gawa a ƙarƙashin shugabancin Damagum – Dino Melaye

Date:

Tsohon Sanatan Kogi ta Yamma, Dino Melaye, ya sake kaddamar da wani mummunan hari kan jam’iyyar PDP, inda ya caccaki shugabancin ta cewa, ta kusan zama gawa.

 

Melaye a ranar Lahadi ya ce, iyayen da suka kafa jam’iyyar kamar Alex Ekwueme, Solomon Lar, Sunday Awoniyi, Adamu Chiroma, Tony Anenih, da kuma Abubakar Rimi za su juya kabarinsu kan abin da mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iliya Damagum, ke yi wa jam’iyyar.

 

Ya yi nuni da cewa tsohuwar jam’iyya mai mulki a yanzu ta zama tambari a karkashin jagorancin Damagum, Samuel Anyanwu, da Umar Bature.

 

A jiya tsohon dan majalisar ya zargi Damagum, Anyanwu, da Bature da ruguza tsohuwar jam’iyya mai mulki.

 

Melaye ya ce sarakunan uku sun lalata jam’iyyar PDP ba tare da wata tangarda ba.

 

Ya kuma zargi jiga-jigan jam’iyyar PDP da yin kasuwanci da mayar da jam’iyyar adawa.

 

A cikin sabon harin da ya sake kaiwa, Melaye ya wallafa a kan X: “PDP ita ce kawai jam’iyyar da ta tsira a jamhuriya ta 4. Bayan shekaru 27.

 

“Alex Ekwueme, Solomon Lar, Sunday Awoniyi, Adamu Chiroma, Tony Anenih, Abubakar Rimi, da dai sauransu za su juya cikin kabarinsu ganin abin da Damagun, Ayanwu da Bature ke yi na burin gina jam’iyyar kasa. PDP yanzu

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp