Jam’iyyar PDP a jihar Abia da ke kudu, ta zabi Okey Ahiwe a matsayin sabon dan takara na kujerar gwamna a zaben da za a yi a wata mai zuwa.
Ahiwe ya lashe zaben fitar da gwani da aka gudanar a birnin Umuahia inda ya doke mataimakin gwamnan jihar Ude Oko-Chukwu.
Karanta Wannan: Dalilin da ya sa muka yi wa Ben Ayade hayaki fidda na kogo – PDP
Ya maye gurbin Uche Ikonne wanda ya rasu a ranar 25 ga watan Janairu.
Kamfanin dillanci labarai na Najeriya – NAN ya ba da rahoton cewa Mista Ahiwe ya samu kuri’a 469 sai kuma Oko-Chukwu da ya zama na biyu da kuri’a 12 kamar yadda Lucky Igbokwe shi ma ya samu kuri’a 12.