Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan, a ranar Litinin ya sake yin kakkausar suka ga jam’iyyar adawa ta PDP, inda ya yi zargin cewa jam’iyyar a lokacin da take mulki ta yi watsi da Arewa maso Gabas ga Boko Haram.
Lawan ya ce, sai da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya hau mulki a karshe aka kwato yankin daga hannun mayakan Boko Haram.
Daga bisani Lawan ya godewa shugaba Buhari bisa dimbin alfanun da yankin Arewa maso Gabas ya samu daga gwamnatin sa.
Da yake jawabi a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC wanda shugaba Buhari ya halarta a Bauchi, shugaban majalisar dattawan ya ce: “Mai girma shugaban kasa, jam’iyyar PDP ta watsar da yankin Arewa maso Gabas ga Boko Haram, wajen tayar da zaune tsaye.
“PDP ta yi watsi da mu har sai da kuka shigo ofis. A 2015, lokacin da aka rantsar da ku, aikinku na farko shi ne ku ‘yantar da mu. Na gode sosai da kuka yi.
Ya ci gaba da cewa: “Mu a Arewa maso Gabas tabbas ne muka fi cin gajiyar gwamnatin ku. A gaskiya mu ne muka fara fara jin dadin mulkin ku fiye da kowane yanki na Najeriya, domin a fasahance an fatattaki Boko Haram nan da nan bayan da kuka hau ofis, kun nada danmu Shugaban Hafsan Sojoji Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai. sannan kuma, Air Marshal Sadique Baba Abubakar a matsayin babban hafsan sojin sama.
“Sun yi kyau sosai har gwamnatin ku ta ba da tsaron da muke samu a yau. Arewa maso gabas, daga 2015 musamman, sun ji daɗin nade-nade mafi mahimmanci a cikin gwamnatin ku. Wato kai dan arewa maso gabas ne. Wannan taron shaida ne. Duk inda ka je sai Buhari, a arewa maso gabas.”
Lawan ya yi irin wannan sanarwar ne makonni biyu da suka gabata a wani gangamin yakin neman zabe a Yobe inda ya zargi PDP da kyale rikicin Boko Haram ya barke a lokacin da jam’iyyar ke mulki.