fidelitybank

PDP ta yi Allah wadai da lalata mata kadarori a Zamfara

Date:

Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara, ta yi Allah-wadai da kakkausar murya dangane da lalata motocin yakin neman zabenta da wasu kadarori da wasu ‘yan daba da suka yi a yayin taron jam’iyyar na ranar Litinin.

Jam’iyyar ta koka da yadda gangamin da jam’iyyar adawa ta PDP ta fara a jihar a ranar Litinin din da ta gabata ya jawo barna mai yawa ga jihar ta hanyar ayyukan ‘yan daba.

Da yake yiwa manema labarai jawabi a ranar Laraba a Gusau, babban birnin jihar, sakataren yada labarai na jam’iyyar APC, Malam Yusuf Idris Gusau ya ce zuwan dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Dr. Dauda Lawal Dare cikin jihar ya sanya ‘yan daba suka kaddamar da hare-haren ta’addanci kan ‘yan kasa da kadarorin da ba su ji ba ba su gani ba. .

“Wannan ya bayyana ne a ranar Litinin lokacin da ‘yan barandan PDP suka tare wata mota da aka makala hotunan Gwamna Matawalle, suka lalata ta kafin su kona ta.

“Daya daga cikin wadanda suka kona kone-konen, Yusuf Aminu ya ce ya yi abin da ya yi ne biyo bayan umarnin da dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, Dauda Lawal Dare ya ba su na kona dukkan tambarin jam’iyyar APC da ke dauke da motoci a jihar.

“Wanda ake zargin, Yusuf Aminu daga Gangaren ‘Yar Rumfa da ke unguwar Gusau ta wani faifan bidiyo ya shaida wa ‘yan sanda cewa ya aikata hakan ne domin gamsar da dan takararsa Dauda Lawal Dare.

“Mu a jam’iyyar APC kullum muna kira da a kwantar da hankula domin a samu zaman lafiya amma wannan abin bakin ciki ya wuce gona da iri kuma ana kallonsa a matsayin wata alama ta raunin tsarin mulki.

“Muna so mu yi gargadin cewa abin da ya faru ya zama na karshe da PDP ko wasu bata gari da ke daukar nauyinta za su yi mana haka,” in ji shi.

Amma da aka tuntubi shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Hon. Mukhtar Lugga ya ce jam’iyyar APC tana neman kasa ne kawai domin a fili take cewa jam’iyya mai mulki ta gaza wa jama’a.

A cewarsa, “PDP ba ita ce matsalar Jihar ba, APC ce,” yana mai jaddada cewa taron ya gudana cikin lumana, kuma an gargadi magoya bayansu da su kasance masu bin doka da oda.

Ya bayyana cewa abu ne mai yiyuwa shugabannin APC su lalata kadarorinsu su dora laifin a kan ‘ya’yan PDP da ba su ji ba su gani ba.

“Suna iya kirkirar karya don su tausayawa jama’a domin sun san cewa jama’a za su yi wa jam’iyyar tawaye ta hanyar akwatin zabe. Suna azabtar da mutanen da ba su ji ba ba su gani ba ne don su samu kuri’u na tausayawa,” in ji shi.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp