Kwamatin gudanarwa na jam’iyyar PDP, ya ɗage lokutan da ya shirya gudanar da wasu zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar kafin babban zaɓe na 2023.
Wata sanarwa daga Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa, Debo Ologunagba, ta ce, za a gudanar da zaɓukan kujerar gwamna ranar Litinin, 23 ga watan Mayun 2022, yayin da za a yi na sanatoci ranar Asabar, 21 ga Mayun.
Zaɓukan ‘yan majalisar wakilai za su gudana ranar Juma’a, 20 ga Mayu, sai kuma na ‘yan majalisar jiha da za a yi Laraba, 18 ga watan na Mayu. Haka nan an ɗage taron zaɓar wakilai wato daliget a dukkan ƙananan hukumomi na ƙasa amma sai nan gaba za a faɗi ranar gudanar da su.
Sai dai sauyin bai shafi zaɓen fid da ɗan takarar shugaban ƙasa ba, wanda tun farko aka tsara yin sa ranar 28 zuwa 29 ga Mayu.