Jam’iyyar PDP ta fitar da tikitin takarar shugaban kasa a ga ƴaƴan jam’iyyar gabanin zaben 2023.
Wannan shi ne sakamakon taron kwamitin zartaswa na kasa (NEC) a jiya wanda aka fara da karfe 8 na dare a ka kuma kammala da karfe 10:20 na dare.
Kwamitin taron jam’iyyar kuma zai kasance karkashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa David Mark.
An tattaro cewa hukumar zaben ta amince da gudanar da zaben fidda gwani a Abuja a ranar 28/29 ga watan Mayu kamar yadda aka tsara tun farko.
Wannan shi ne sakamakon taron hukumar zaben da aka gudanar a jiya wanda aka tattauna kan rahoton kwamitin shiyya 37 da gwamnan jihar Benue Samuel Ortom ya jagoranta.