Jam’iyyar PDP ta zabi Sanata Danjuma La’ah (PDP-Kaduna) a matsayin mataimakin mai wakiltan marasa rinjaye na majalisar dattawa.
Hakan na kunshe ne a cikin wata wasika mai dauke da sa hannun sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Samuel Anyawu zuwa ga shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan kuma aka karanta a zauren majalisar ranar Laraba.
Mista Anyawu ya ce, an zabi La’ah ne domin maye gurbin tsohon bulaliyar majalisa na marasa rinjaye, Sanata Ibrahim Danbaba wanda ya koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
“Muna fatan tabbatar da zaben Sanata Danjuma La’ah da jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) Majalisar Dattawa ta yi, domin cike gurbin kujerar dan majalisar dattawa.
“Nadin La’ah ya biyo bayan sauya sheka da Sen. Ibrhaim Danbaba tsohon mataimakin jam’iyyar PDP ya yi zuwa APC.