Kwamitin tantance ‘yan majalissar dokokin jam’iyyar PDP a jihar Kogi, ya kori Ubolo Itodo Okpanachi da Aminu Abubakar Suleiman daga takarar Sanatan Kogi ta Gabas bisa wasu ayyuka na rashin da’a.
Sakamakon tantancewar da aka fitar a ranar Alhamis a Lokoja, babban birnin jihar, ya nuna cewa, yayin da Isaac Alfa da Victor Adoji suka samu takardar amincewar kwamitin don ci gaba da neman kujerar sanata, Suleiman da Okpanachi an hana su shiga takarar.
Suleiman dai an tantance shi ne kuma ba shi da rajista katin jam’iyya a yankin majalisar dattawa, don haka bai cancanci shiga zaben Sanata ba.
An ce kwamitin ya lura da cewa rashin cancantar kada kuri’a ko kuma shiga zaben ‘yan majalisar dattawa, kai tsaye ya toshe damarsa na cin gajiyar duk wata kuri’a da aka kada a gundumar. Suleiman, ya kara da cewa kwamitin bai zabi kowa ba a Kogi ta gabas don haka bai cancanci tsayawa takara ba.
A daya bangaren kuma, Okpanachi, ba’a wanke shi ba, saboda zarginsa da hannu a cikin ayyukan kin jinin jam’iyya da kuma tarin wasu korafe-korafe da ke kalubalantar cancantar sa na tsayawa takara.
Ana zargin sa da zama dan jam’iyyar APC, jam’iyyar da aka ce ya koma, kuma a wani lokaci aka ba shi mukami.