fidelitybank

PDP ta kori Dan Majalisar wakilai daga Imo

Date:

Babbar jam’iyyar hamayya PDP, ta kori wani dan majalisar wakilai daga Jihar Imo, Ugochinyere Ikenga, daga jam’iyyar.

Mista Ikenga, wanda ke wakiltar mazabar Ideato North-South a ajalisar wakilai, shi ne mai magana da yawun kungiyar hadin kan jam’iyyun siyasa (CUPP), kuma an kore shi ne bisa zargin rashin da’a da ayyukan da suka saba wa jam’iyyar.

Mai magana da yawun PDP a Jihar Imo, Lancelot Obiak, ya bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a cewa shugabannin jam’iyyar na karamar hukumar Ideato North ne suka yanke hukuncin korar Mista Ikenga.

“Korar ta biyo bayan rahoton kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar ne, mai dauke da kwanan wata 27 ga Nuwamba, 2024, wanda ya gudanar da bincike kan zarge-zargen rashin da’a da ake yi wa Ugochinyere, bisa tanadin Sashe na 57 (1-4) na kundin tsarin mulkin PDP na 2017 da aka gyara,” in ji Mista Obiak.

Ya ce shugabannin PDP na karamar hukumar Ideato North sun zargi Mista Ikenga da aikata manyan laifukan rashin ladabi, ƙin bin umarni, da kuma ayyuka masu ma’ana da suka ci karo da manufofin jam’iyyar.

“Tun da farko, an dakatar da ɗan majalisar a matakin mazabarsa ta Umuopia/Umukegwu a ranar 14 ga Oktoba, 2024, bayan ya ƙi amsa gayyatar kwamitin shugabannin mazabar a ranar 5 ga Oktoba, 2024, don amsa zarge-zargen rashin da’a.

Har ila yau, ya ƙi mayar da martani kan tunatarwa da ƙarin gayyata da aka tura masa a ranar 7 ga Oktoba, 2024,” in ji Obiak.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp