fidelitybank

PDP ta kori Dan Majalisar wakilai daga Imo

Date:

Babbar jam’iyyar hamayya PDP, ta kori wani dan majalisar wakilai daga Jihar Imo, Ugochinyere Ikenga, daga jam’iyyar.

Mista Ikenga, wanda ke wakiltar mazabar Ideato North-South a ajalisar wakilai, shi ne mai magana da yawun kungiyar hadin kan jam’iyyun siyasa (CUPP), kuma an kore shi ne bisa zargin rashin da’a da ayyukan da suka saba wa jam’iyyar.

Mai magana da yawun PDP a Jihar Imo, Lancelot Obiak, ya bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a cewa shugabannin jam’iyyar na karamar hukumar Ideato North ne suka yanke hukuncin korar Mista Ikenga.

“Korar ta biyo bayan rahoton kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar ne, mai dauke da kwanan wata 27 ga Nuwamba, 2024, wanda ya gudanar da bincike kan zarge-zargen rashin da’a da ake yi wa Ugochinyere, bisa tanadin Sashe na 57 (1-4) na kundin tsarin mulkin PDP na 2017 da aka gyara,” in ji Mista Obiak.

Ya ce shugabannin PDP na karamar hukumar Ideato North sun zargi Mista Ikenga da aikata manyan laifukan rashin ladabi, ƙin bin umarni, da kuma ayyuka masu ma’ana da suka ci karo da manufofin jam’iyyar.

“Tun da farko, an dakatar da ɗan majalisar a matakin mazabarsa ta Umuopia/Umukegwu a ranar 14 ga Oktoba, 2024, bayan ya ƙi amsa gayyatar kwamitin shugabannin mazabar a ranar 5 ga Oktoba, 2024, don amsa zarge-zargen rashin da’a.

Har ila yau, ya ƙi mayar da martani kan tunatarwa da ƙarin gayyata da aka tura masa a ranar 7 ga Oktoba, 2024,” in ji Obiak.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp