Jam’iyyar PDP ta shigar da kara a gaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), a kokarinta na hana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Bola Tinubu da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP) Peter Obi zaben Kashim Shettima da Datti Baba-Ahmed a matsayin abokan takararsu.
Jam’iyyar PDP ta kuma bukaci kotu ta yanke hukuncin cewa, Kabiru Masari da Doyin Okupe, Tinubu da Obi na tsaffin abokan takarar su ne kowannen su ya samu damar tsayawa takara shi kadai.
Jam’iyyar PDP na neman kotu da ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta daga sauya abokan takarar Tinubu da Obi a cikin sammacin farko mai lamba FHC/ABJ/CS/1016/2022.
A wannan yanayin, INEC, APC, Tinubu, Masari, Labour Party, Obi, da Okupe sune wadanda suka amsa na farko zuwa na bakwai.