fidelitybank

PDP ta jinjina wa sojojin Najeriya a fagen daga

Date:

Jam’iyyar hamayya ta PDP, ta jinjina wa sojojin Najeriya, bisa jajircewa da sadaukar da kai da su ke yi a ƙasar nan, musamman a lokacin da ta fuskanci tabarbarewar tsaro a cikin shekaru shida da suka gabata.

Jam’iyyar PDP ta yi na’am da irin bajinta da kishin kasa da jiga-jigan sojojin ke yi a fagen daga, wadanda duk da kalubalen da ake fuskanta a kullum, suna jefa rayuwarsu cikin kangi, inda da yawa suke rasa rayukan su, domin hadin kai da tsaron Najeriya.

PDP ta bayyana hakan ne a lokaci bikin tunawa da ƴan mazan jiya wanda aka gudanar a ranar Asabar.

Jam’iyyar PDP, ta kuma bukaci gwamnati ta dauki matakin samarwa sojojin isassun kayan aiki tare da inganta jin dadin sojojin, domin tabbatar da ingancin aikinsu ga ƙasa.

Ta ce, “Jam’iyyar mu kira ga gwamnati da ta tabbatar da jin dadin iyalan jaruman mu wadanda suka sadaukar da rayukansu, domin al’ummarmu. Kar a bar iyalansu da ‘yan uwansu su ci gaba da shan wahala”. A cewar PDP.

Jam’iyyar PDP ta kuma bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da bayar da goyon baya da kuma yi wa sojoji addu’a a babban aikinsu na kare ƴan Najeriya.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp