fidelitybank

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Date:

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP na ci gaba da tattanawa wajen gani sun shawo kan ɓarakar da ta kunno kai a tsakaninsu da ya janyo tsaiko, wajen gudanar da taron majalisar zartawa na jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a yau Litinin.

Tun da safiyar yau ne dai aka ga jami’an ‘yansanda da na tsaron fararen hula na Civil Defense suka yi wa ofishin jam’iyyar na Wadata Plaza, Abuja tsinke tare da hana dukkanin manyan jami’an jami’yyar shiga.

Yanzu haka dai kwamitin amintanntu na jam’iyar na gudanar da wani taron sirri a babban ɗakin taro na Ƴar’adu Center da ke Abuja.

Taron nasu na zuwa a daidai lokacin da gwamnonin jam’iyyar da ƴan majalisar dattawa da na wakilai da ke gudanar da wani taron a gidan gwamnatin jihar Bauchi da ke unguwar Asokoro a birnin na Abuja.

Wakilin BBC da ke wurin ya ce duka tarukan biyu ana yi ne da nufin lalubo bakin zaren yadda za a gudanar da babban taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar (NEC) da ake shirin yi a ofishin jam’iyyar da ke Wadata Plaza.

Tun da faro dai kwamitin Amintattun Jam’iyyar sun shirya gudanar da taron nasu ne a ofishin jam’iyyar da ke Wadata Plaza da misaƙalin ƙarsfe 10:00 na safe amma hakan bai samu ba.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp